Abokin Aikina Book 1 Page 11

 


LAMBA SHA ƊAYA.*


         _A ranar da na fara haɗuwa da shi, ina kan hanyar zuwa Bafarawa estate na fito Line G. Inda na kai wa wata ƙawar mahaifiyata ziyara a bisa umurnin ta. Domin ɓeran masallaci ce ni babu inda nake zuwa kullum ina gida, wannan fitar ma ta matsa ne sai na je na gayar da danginta da ke Dunguza, saboda babu tazara tsakanin su da Line G . Kullum suna ƙorafin ba ta bari na yi

zumunci, idan na zo har na koma ba su sani ba. Su yi ta mita bayan sun juye laifin da nufin ita ce ba ta so na yi zumunci da su._

        _Kasancewar ba wata tazara ce mai yawa ba, na zaɓi komawa ƙasa domin na miƙa ƙafafuwana. Na fito Line G. Kenan daidai polo na ji magana a bayana, cikin sauri na waiga na yi tolazi da fuskar shi ɗauke da murmushi. Amma tun daga kallo ɗayan da na yi masa ban sake bi ta kan shi ba, tafiya nake yi yana bi na a baya yana faɗin,"_

       "Don Allah ki tsaya ki saurare ni, unguwarku kawai nake so ki sanar da ni sai lambar wayarki".

         _Na ci gaba da tafiyata ban tsaya ba balle na tanka shi kamar yadda yake so. Tun yana yi mini magiya ina jin haushin takurar da ya yi mini har ta kai ya fara ba ni tausayi. Saboda muryar kukan da na ji ya koma yi cikin marairaitar da ya yi nasarar saka ni tsayawa na ce da shi,_

       _"Ka yi haƙuri ba na magana a kan hanya..."_


       "Lambar wayarki kawai nake so ki ba ni. Sannan ki sanar da ni a ina zan same ki?"


     _Tafiya na ci gaba da yi ya biyo ni yana ci gaba da roƙon lambata amma ban sake bi ta kan shi ba, har na isa gidansu Ummata da ke Bafarawa estate._

        _Kwana biyu tsakani ina tsaka da aiki aka aiko wani yaro ana kira na, ina gunguni haɗi da tsaki na fito. Saboda takurar da Umma ta yi mini a kan dole sai na je na ga wanda ke nema na. Da mamaki na bi shi da kallo saboda tunanin wa ya sanar da shi unguwar balle gidan da nake. Murmushi ya bi ni da shi hannun shi a aljihu ya ce,_

           "Kin yi mamakin gani na ko? To Hausawa sun ce mai son ɗan tsuntsu shi yake bin shi da jifa, shi ya sa na biyo sawunki sau da ƙafa har na ga gidan. Saboda na gani kuma na yaba da kalar tarbiyyarki. Hakan da kika ya ƙara miki matsayi a zuciyata da ƙima a cikin idanuwana. Don haka ga Muhammadu Mukhtar da fatar ya yi miki a matsayin mijin auren ki!".


     _Shiru kawai na yi domin har zucina natsuwar shi ta burge ni, sai dai a lokacin ba aure ne a gabana ba domin farkon shiga ta Jami'a kenan. Kuma ina da burin karatun shi ya sa ba na kula samari ko a Kebbi duk da takurar da suke yi mini. Don asali ma akwai wani da muke soyayya da shi sai dai Baba Ali bai yi na'am da shi ba. Hakan ya sa duk nacin da yake yi a kan ya turo Iyayen shi a tsayar da magana bai amince da hakan ba. Dalilin da ya sa na fuskanci karatun da kyau domin na samu abin da na je nema._


     _Ajiyar zuciya na sauke sannan na ce,_ "Ka yi haƙuri da abin da na yi, saboda ba na tsayawa magana a titi. Musamman irin Polo club da ta zamo mahaɗar kasuwanci da dandazon mutane..."

       "Hakan ma ya tabbatar mini na yi zaɓen matar aure a inda ya dace. Amsar ki kawai nake buƙata yanzu domin ita ce abu ma fi muhimmanci a wurina". 


     _Shiru muka yi daga ni har shi ina wasa da gefen hijabina amma jikina a mace saboda daburcewar da na yi na rasa me zan ce. Ga kuma jikina ya ba ni idon shi duka a kaina suke, na yi jarumtar ɗagowa domin na saci kallon shi. Caraf muka haɗa idanuwa na yi saurin janye nawa ina masa kallon gefen ido, amma shi kafe ni ya yi da kallo ko ƙyaftawa ba ya yi. Na kawar da kaina gefe tare da rungume hannu a ƙirji na ce,_ 

      "Ka ba ni lokaci zan sanar da kai idan na gama shawara". 

       Shiru ya yi na ɗan lokaci sannan cikin sanyin murya ya ce, "Kamar zuwa yaushe za ki gama shawarar?"

"Sati ɗaya"

Na ba shi amsa ina ɗan murmushi, ya maraice murya yana faɗin "Kafin lokacin na zama gawa ai". 


     _Dariya ta suɓuce minu saboda sosai zancen shi ya ba ni dariya, domin yanayin da ya yi maganar yana karye wuya tamkar yaron da aka ƙwace wa alawa yana tsaka da jin zaƙinta._

      "Kwana uku ai ya yi ko?"


"Kwana ɗaya tak zan iya juriya, ko shi zan kasance cikin wasiwasi da ƙididdigar lokaci. Don haka ki taimake ni ki sanar da ni yanzun nan ko don na fita fargabar da nake ciki..."

     "Ka kwantar da hankalinka in Sha Allah alheri ne". 


_Daga haka ya ci gaba da ja na da hira har duhun magrib ya kawo jiki. Sallama muka yi da shi bayan na ba shi lambar wayata, domin ya kira ya ji amsar shi gare ni._


***

      _Abu kamar wasa soyayya mai ƙarfi ta shiga tsakanina da Mukhtar. Saboda ƙarfin da Umma take ƙara wa abin a ƙoƙarinta na son na yi aure Sokoto ko don na dawo kusa da ita. Amma Baba Ali bai karɓi abin kamar yadda Umma ta ɗauke shi da muhimmanci ba. 

Familyn su Mukhtar sananne a cikin garin Sokoto, shi ya sa ba a sha wuya ba yayin binciken asalin shi, wane ne shi a idon mutane._


      _An ɗauki lokaci muna soyayya da Mukhtar, kuma Baba Ali bai hana shi zuwa wurina ba kamar yadda ya yi mini iyaka da Jafar. Saboda ya nuna ƙarara ba zai ba shi ni ba, saboda asalin tushen shi Rundawa ne su. Kuma a cewar shi abin kunya ne da Allah-wadai ga Bafulatanin da ya haɗa zuri'ar shi da masu Fawa. Duk da wasu daga cikin 'yan'uwanmu sun tunatar da shi Allah bai haramta ba, amma ko kaɗan bai yi amanna da hakan ba. A ƙarshe ma fitowa ya yi a fili ya sanar shi ya yi mini miji ya yi haƙuri._

     _Sosai na ji tausayin Jafar saboda na san kalar son da yake yi mini marar algus. Duk da a lokacin ni kaina zuciyata ta fi karkata da son Mukhtar fiye da shi. Dalilin hakan na tattara shi gabaɗaya na ajiye gefe, na bai wa Mukhtar matsayi mai girma a raina. Bayan lokacina da na sadaukar masa, amma ban bari ƙaunar da nake yi masa ta shafi karatuna ba. Kasancewar doka ce ta musamman Baba Ali ya gindaya mini, duba da yadda na yi nisan kiwon da ba na jin kira a kan soyayyar Mukhtar._


***

    _Zancen aure na da Mukhtar ya kankama har an kawo sadakina. Domin ƙa'ida ce a wurin Baba Ali ba ya bari a yi wa 'ya'yan shi lefe, duk da yake ɗan boko kayan fitar biki kawai yake ɗora wa wanda zai auri 'yar shi. Saboda ba a kaina aka fara ba shi ya sa ban wani damu ba. Amma Ummata ta ji haushin hakan kasancewar ni kaɗai ce gare ta har lokacin. Duk da ta yi aure biyu bayan mutuwar Babana amma babu inda ta haifu._

 _Mukhtar ya nuna mini jin haushin shi sosai dangane da soke lefen da Baba Ali ya yi. Domin ya sanar da ni har ya gama haɗa komai lokacin kawo mini kawai ya rage a saka, amma hakan ba zai hana shi ajiye mini ba idan na zo sai ya ba ni. Na yi farinciki sosai da maganar ta shi, kuma zuciyata ta ƙara tabbatar mini ƙololuwar ƙaunar da yake yi mini. Ummata ma ta ji daɗi a lokacin da ta ji labarin lefe na zai tarbe ni a gidan Mukhtar._


    _Ba a yi bikin ba sai da na kammala digirina, amma tun a lokacin ya nuna mini ba zai bari na yi aiki ba. Kasancewar ina son shi ban kalli hakan a matsayin wani abu ba. Baba Ali ma da ya yi masa zancen aikin ni na ba shi shawarar ya ce masa ya amince. Saboda gudun matsala ta biyo baya ga shi a lokacin ba zan iya juriyar rashin shi ba. Kuma hakan ta kasance a lokacin da ya kira shi takanas domin su yi magana a kan aikin nawa. Baba Ali ya ji daɗin hakan kuma ya ƙara nuna farincikin shi a kan halin yakamatan da ya hango ga Mukhtar._


      _Sadaki sai kayan fitar biki kala biyar Mukhtar ya gabatar a yayin neman aurena. Aka yi bikinmu cikin mutunta juna aka kai ni gidan su Mukhtar da ke unguwar Sokoto Silma. 'Yan'uwan shi da abokan arziƙi duk wanda ya gan ni sai ya ce ma sha Allah, saboda kyakkyawar halittar da Allah ya mallaka mini. Kasancewa ta farar bafulatana mai dirarren jiki da yalwar faffaɗan ƙugu ga cikar ƙirji._ 

    

***

_Daren ranar babu komai da ya shiga tsakanina da shi, kasancewar wasu daga cikin ƙawayena da danginmu na Kebbi a nan suka kwana. Sai ta ta biyu ya karɓi budurcina ba tare da na san me ya faru a lokacin ba. Domin har yanzu da nake bayar da labari ba zan iya kawo me ya faru a darena na farko da Mukhtar ba. Da asuba na farka na tsinci kaina cikin sabon sauyi, tuna abin da ya faru ni da ni kafin ya shiga jikina. Ya sa na rufe fuskata cike da jin kunyar kaina a cikin idanuwana. Na miƙe ban gan shi a ɗakin ba na yi toilet ɗinmu da ke cikin ɗakin, tsarkake jikina na yi sannan na yi wankan tsarki na fito. Sallaya na shimfiɗa na yi sallah na yi addu'o'in zaman lafiya ni da angona Mukhtar. Sannan na yi karatun Qur'ani da na gama na yi azkar ɗina kamar yadda na saba. Domin gidan Baba Ali ba a wasa da sallah sosai ake riƙo da addinin Islama. Mun samu ilimin muhammadiyya daidai gwargwado, mun yi saukar Qur'ani kuma mun haddace littafai da dama._ 


     _Rayuwar amarcina da Mukhtar gwanin ban daɗi, duk da ina shan mamakin yadda ba ya barin kuɗi a hannuna. Duk abin da aka ba ni shi yake karɓewa, kuma ba na jin ko ɗar haka zan miƙa masa. Saboda ina tunani tara mini yake yi gudun a sace, duba da yadda gidan yake cika da mutane koyaushe ana zaryar zuwa ganin amarya da muhallinta. Domin babu abin da ba a yi mini na 'ya'yan gata ba, kayan ɗakina ma abin kallo ne bayan ƙattin kujeruna da suka canye filin falon. Bayan firij da sabuwar telar da aka haɗo ni da ita, domin na nemi na kaina kafin na fara aiki._

   _Har a raina ina so na yi alheri ko da kuɗin abin hawa ne idan dangin Ummata suka zo wurina, amma babu ko ficika a hannuna. Sai idan an yi katari yana gidan na tambaye shi ya ba ni na ba su._


      _Ashanar da nake tsinta a cikin ɗakina ko falo lokaci bayan lokaci, ita ce abu na farko da ya fara ɗaure mini kai a gidan Mukhtar. Tun ba na kula har na fara tambayar shi ko shi yake ajiye ta, amma ya nuna mini shi ma bai san da ita ba. Cikin tsoro nake tofe ashanar da addu'a sannan na ɗauke ta na kai na ajiye, abin mamaki kuma sai na nemi ashanar inda na ajiye na rasa. Idan na tambaye shi shi ya ɗauka ya ce da ni a'a, tun ina bi ta kai har na watsar ina ci gaba da addu'o'in tsari saboda ina da tsoro sosai._


    _Matsala ta farko da na fara cin karo da ita a wurin Mukhtar ita ce rashin tashi sallar asuba. Ba ya yin salla sai ya yi wanka idan zai fita wurin aiki, wani lokaci har ƙarfe takwas da rabi yana kai wa bai yi sallar asuba ba. Abin ya fara damuna na fara yi masa ƙorafi a kan hakan, saboda duk na tashi sallar asuba sai na tayar da shi amma ya ƙi tashi. Wani lokaci ma tsaki yake yi ya juya kwanciyar shi ba tare da ya tashi ba._

       _Tun yana jin haushin takurar da nake yi masa har ya fara tashi yana yi ba don yana so ba, don wani lokaci ma har ya tafi wurin aikin shi yana fushi ba ya sake mini fuska. Abin yana ba ni mamaki sosai duba da masallacin da ke ƙofar gidansu, wanda kira da Sallar shi duka ina ji tar-tar har cikin ɗakina._


  ***

_Watana ɗaya da sati biyu gidan Ummata da matar Yayanta suka zo ganin ɗakina. Saboda tsabar murnar ganin su bakina har kunnena, na tarye su da abin da nake da shi sannan na kira shi na sanar da shi zuwan su. Mintuna a tsakani ya zo da kayan marmari da jiƙa maƙoshi, na saka musu a tire na ajiye gabansu suna gaisawa da shi. Kan shi a duƙe cikin tsantsar ladabi har suka gama ya fice, na gabatar musu da abin taɓa bakin muka fara hira. Matar Kawuna ta shiga binciken zamanmu a fakaice na sanar da su komai lafiya, domin su tabbatar da abin da suka ce sun ji a bakin mutane. Dangane da zaman lafiyar da ke tsakanina da Mukhtar. Domin duk wanda ya zo ba ya gani na cikin baƙar fuska balle rashin walwala, hakan ne yake nuna zaman lafiya da jin daɗin aurena a zahiri._ 

       "Zaituna ya zancen lefenki! Mun yi ta jira mu ji kin kira mu zo mu gani amma har yanzu babu labari. Ko dai ya ba ki mu ne ba ki faɗa ma ba?" 

      _Maganar Inna Kulu kenan domin ta ji ba'asi a kan lefen da ni ma nake bitar zancen shi cikin raina koyaushe. Domin na kasa yi wa Mukhtar tuni a kan lefen, saboda ba na so ya ga na cika zalama. Shi ya sa na dakata domin na ga zurfin gudun ruwan shi. Tambayar da Inna Kulu ta yi ta fama mini damuwar abin a raina, amma na bagayar da faɗar,_

        "Ko jiya mun yi zancen ya ce na ƙara haƙuri kwanan nan Iyayen shi za su kawo mini".

      "Ma Sha Allah! To Ubangiji ya ƙara muku zaman lafiya da fahimtar juna. Idan suka kawo ki  sanar da mu cikin lokaci domin a san me za a bayar tukuici". 


_Dariyar yaƙe kawai na yi tare da ɗaga kai, cike da fargaban kada Mukhtar ya sa na ji kunya a kan ƙaryar da na yi musu, domin na ƙare masa martabar shi a idanuwansu. Lokacin da za su tafi na kira shi ya ba ni ɗari biyar na ba su, shi kuma ya ba su dubu biyu suka ce ba za su karɓa ba. Da ƙyar na matsa suka karɓa ko shi sai da ya fice sannan suka karɓa a hannuna._ 


      _Da dare lokacin da muka kwanta bacci yana wasa da jikina nake yi masa tambaya a kan lefen, nesa da ni ya koma ya juya mini baya bai ce da ni komai ba. Shiru ya ratsa tsakani sai tashin minsharin shi na ji alamun ya yi bacci. Na ɗauki lokaci ina tunanin abin da ya sa ya yi mini haka daga tambaya, ban san lokacin da bacci ya yi awon gaba da ni ba._

     

No comments

Powered by Blogger.