Abokin Aikina Book 1 Page 10


*LAMBA TA GOMA.*


       Cikin sauri ya yi gefe wayar a hannun shi yana dubawa, haushi ya sa na bar shi da wayar na dawo na zauna ina ci gaba aikina. Sai da ya gama binciken abin da yake son gani, sannan na fara jin maganganun da suka ƙara tunzura ni daga bakin shi. 

      "Wai ke har yaushe za ki gano aure yana da muhimmanci? To wallahi a wannan karon zan ɗauki mummunan mataki a kan wannan munafukin mutumin..."

      "Kafin ka ɗauki mataki a kan shi, ka fara ɗauka a kanka domin abin kunya da Allah wadai ba halin shi ba ne shi. Don haka ka yi duk abin da ka ga za ka iya tun da shi kwando yana iya ce wa rariya na yoyo". 


     A fusace na ba shi amsa, shiru ya ratsa a tsakani ba tare da ya ce komai ba. Ban ɗago ba balle na ga yanayin shi, amma jikina ya ba ni kallo na yake. 

         "Yanzu don Allah ke ba za ki mutunta auren da ke kanki? Babu hujjar da za ki riƙa balle ki halasta tarayyar da kike yi da wannan ƙaton mutumin. To bari ki ji abin da ba ki sani ba, wallahi idan na lamunci komai ba zan yarda da irin wannan cin kashin ba. Don haka zan ɗauki mataki a wannan karon tun da ke ba ki san zurum ba..."

       "Ka riga da ka yi sake ɗan zaki ya girma, a yanzu na riga da na ƙuna ba na tarar ƙauri. Duk abin da za ka yi wallahi a jiraye nake domin babu abin da zai razana ni..."

 "Haka kika ce?"

 "Haka na faɗa!"

        Fuu! Na ji ya wuce ba tare da ya ba ni wayar ba,  na yi hanzarin ajiye rubutun na sha gaban shi cikin matsanancin fushi na ce, "Ba ni wayata!" 

"Ba zan bayar ba...!"

     Amsar da ya ba ni kenan bai gama rufe bakin shi ba, cikin azama na fara ƙwatar wayar ta ƙarfi a hannunshi. Kokawa muka fara yi da shi ina ƙoƙarin ƙwata yana hana ni, a bisa tsautsayi ya ɗaga wayar sama na yi zillo na bugo hannun shi ta suɓuce masa. Cikin zafin nama na yi ƙoƙarin cafko ta amma ban yi dacen hana ta kai wa ƙasa ba.  Kife ta faɗi na duƙa zan ɗauka ya saka ƙafa ya shura ta ta daki bango gabaɗaya ta tarwatse.

      Layina na kawai na duƙa na zare daga jikin kwankwatsattiyar wayar, sannan na juya ba tare da na ce da shi komai ba. Domin a lokacin komai zan iya yi masa ɓangaren aika-aikar da zan illata shi matuƙar na biye zuciyata, gudun aikin da-na-sani a zuci na yi jarumtar faɗar 'Innalillahi wa inn ilairraji'un' Allah ya taimaka na yi controlling temper ta cikin ɗan lokaci. 


     Takardun na kwashe na yi saurin shigewa ɗakina na rufe. Sannan na janyo sabuwar wayar da MD ya ba ni na saka layina da memoryna. Kasancewar akwai nefa a lokacin na jona caji na kwanta ina sauke numfashi a wahale, saboda yadda nake ji tamkar zuciyata za ta ɓalle ta fito a kan matsanancin bugun da take yi. 

        Tsawon lokaci ina cikin mawuyacin halin kafin zuciyar ta lafa numfashina ya daidaita. Ihun yara da bugun da ake yi wa ƙofar ɗakina hakan ya tabbatar mini da yara sun dawo. Daga nan inda nake na yi musu magana cikin ɗaga murya, 

       "Ku je ku yi shirin sallah!" 

       Shirun da na ji ya gasgata sun ji abin da na ce. Ko da aka yi kiran sallar magrib ban tashi ba har sai da aka fara tayar da Sallah. Sannan na miƙa cikin rashin kuzari na yi toilet na ɗoro arwala na yi sallah, na daɗe ina jera addu'o'i a kan Ubangiji ya kawo ƙarshen zamana da Mukhtar lafiya. Domin ba na fatar zuciya ta ɗebe ni na aikata abin da zai shafi mutuncin 'ya'yana na janyo wa Ummata da 'yan'uwana gori.


     Daren ranar ban fita falo ba, a nan na ƙarasa aikin takardun sai da goman dare ta buga, sannan na gama na fito domin na ga a wani hali yarana suke. Addu'a na tofe su da ita sannan rufo musu ƙofa ina goge ƙwallar tausayinsu da ta gangaro mini. 


    Kasancewar ba na cikin walwalar zuciya setting ɗin WhatsApp kawai na yi, sai facebook da na ɗan leƙa bayan na buɗe. Ban wani jima ba na ajiye wayar saboda komai ya gundure ni, idan aka cire MD da ke gefen zuciyata motsi kaɗan sai na tuno shi a raina.


     Da safe ma sai da na canye cikin shigar doguwar rigar atamfa ɗinkin A.shape. Na yafa mayafina mahaɗin atamfar da takalmin da suka yi shige da kalar atamfar. Na feshe jikina da turaruka ba tare da na damu da huduɓar MD ba. domin burin da nake da shi, a kan wani dalili ya yi tsanin haɗa numfashina da na shi ko da tazara ta ratsa tsakaninmu. 

     Kamar jiya har na saukar da yara makaranta ba su daina yabon kwalliyata ba. Duk da ban shafa komai a fuskata ba face powder da lips, sai ɗan kwallin da na zirara wanda sai an kula da gaske ake hango shi idona. 

         Tun a lokacin da na shiga ma'aikatar na fara cin karo da MD ya fito zai nufi motar shi. Ina hankalce da shi kallo ɗaya ya yi mini ya kawar da kai, murmushia a kan fuskata na gaishe shi ƙirjina yana bugawa. Saboda kwarjinin shi ya sa na manta da komai ta yadda ban san lokacin da na saki fuskata ba. 

       Haka na yi ta gaisawa da mutane fuska a sake, duk da kallon hadarin kajin da na ga wata ma'aikaciya tana yi mini. Ban damu ba kuma ban ji haushi ba, domin ba ta gabana tun asali balle na saka ta cikin abubuwa masu muhimmanci. Saboda tun zuwana wurin na fahimci akwai hassadata a cikin zuciyarta, sai ga shi na ji komai a bakin Amina. Ashe mijinta ne aka karɓe wa matsayi aka ba ni, asali ma aka kore shi gabaɗaya cikin ma'aikatar. Dalilin zanba zamba cikin aminci bayan ruf-da-ciki da sama-da-faɗin da yake yi wa kuɗin wurin. Wanɗanda yake wadaƙa son ran shi daga shi har matar shi wadda take matsayin mataimakiyar shi. 


     Ni da ban san lokacin da aka yi ba, amma hakan bai wanke ni daga shiga komarsu ba. Duk inda ta gan ni kallon banza ne ke raba mu, tun ina kula ta sama-sama har na tattara ta na watsar domin ba ta gabana. Surutan da take yi a kaina ma ban taɓa bi ta kai ba, domin ina ji a raina ba ta kai wadda zan ɓata lokacina a kanta ba. 


    Zama na yi a kan kujerar offis ɗina, ina dudduba aikin da na yi ina gyara inda ya dace. Kira ya shigo wayata na yi hanzarin fito da wayar a jaka babu shiri ƙirjina ya buga. Cikin sauri na ɗauka,

       "Ki kawo takardun idan kin kammala aikinsu".


     Zancen MD kenan bai ƙara da komai ba ya katse, cikin sauri na tattara takardun na yi offis ɗin shi. Da siririyar sallama na tura ƙofar na shiga, kaina a ƙasa na ajiye masa takardun zan juya. 

"Shi dai wannan turaren ba za a daina saka shi ba kenan?" 

      Maganar da ya jefo mini kenan cikin ƙasan maƙoshi, shiru kawai na yi masa ina wasa da yatsun hannuna. "A matsayinki na matar aure, bai dace kina bari wani yana shaƙar ƙamshinki ba, wanda na san kin sani ko wadda babu aure kanta ba a halasta mata shafa turare dan za ta fita ba..." 

     "Sai bayan na saka na tuna, amma in Sha Allah zan kiyaye daga wannan". 

       Na ƙare zancen cikin sanyin murya da ƙara mata zaƙi. Bai ce da ni komai ba har na kai ƙofa zan fita na tuno saƙon shi na jiya da ban ga me  ya rubuta ba. Juyowa na yi riƙe da handle ɗin ƙofar cikin ɗakiya na ce,

     "Jiya ban ga saƙon ka ba wayar ta fashe. Ina ƙara godiya Allah ya ƙara buɗi". 

     "Amin" Ita kaɗai ya faɗa ya ci gaba da aikin da yake yi, na fito zuciyata fes saboda kulawar ta shi gare ni.  Hakan ya tabbatar mini da fatsata ta fara kamo mini kifi.


     Ranar ban yi aiki da yawa ba, ina tsaka da chatting Amina ta shigo, muka gaisa fuskarta babu yabo babu fallasa domin na kasa tantance yanayinta.

     Zama ta yi tana sauke ajiyar zuciya ta ce "Jiya da tunaninki na kwana, ta yadda na matsu safiya ta waye na zo domin na ji tarihinki..." 

     "Ina Mama fatan tana lafiya?"

    Tambayar da na yi mata kenan domin na ji yadda suka ƙare da rikicin kwanan. "Ina kwana ce kawai ta haɗa mu yau. Ita ma ba ta amsa ni ba, na ƙara yi mata duk da na san ta ji ni a farko. A masifance ta katsa mini tsawa tana faɗin na bar mata ɗakinta ba ta son gani na. Da na ƙi tashi ta yi kaina da duka na fice, a bisa tsautsayi ta rufo ƙofar ɗakinta cikin fushi ta dantse mini yatsun hannu na. Na jima ina jinyarsu kafin su rage mini zugi na samu ƙarfin fitowa". 


     ""Hmmmmm! Batun kwanan fa a can ya kwana ko a wurinki?" 

     Shiru ta yi tana goge hawaye tsawon mintuna sannan ta ce, "A can ya kwana". 

      "Ki yi haƙuri komai yana da farko kuma yana da ƙarshe. In Sha Allah komai zai zamo tarihi watarana". 


     Daga ni har ita muka yi shiru, na shiga dogon tunanin cutarwar da mata suke fuskanta a gidajen aurensu. Tare da tambayar kaina 'Yaushe ne mata za su daina fuskantar ƙalubalen aure?' 

        'Babu rana' amsar da wata zuciyar ta ba ni kenan cike da tabbacin matuƙar ba a ɗinke ɓarakar ba, to ba za a taɓa daidaituwa tsakanin ma'aurata ba.

 'Ta wace hanya?'

      Tambayar da na sake yi wa kaina a zuciyata kenan, kafin Amina ta katse mini zancen zucin da nake yi, "Ina so ki sanar da ni abubuwan da kika fara faɗa mini jiya, wanda asali dalilin hakan ya sa na fito aiki yau. Domin ba na so na ƙi  zuwa na yi missing wannan babban Flight'".

'Yar dariya na yi saboda ƙarshen zancenta, shiru na yi ina nazarin ta inda zan fara ba ta labarin kaina. 


        _"Kamar yadda kika sani sunana Zaituna Aliyu, amma Aliyu Yayan mahaifina ne ba shi ne asalin wanda ya haife ni ba. Sunan mahaifina Alhaji Sani. Na samo asalin sunan tun a ranar da Baba Ali ya saka ni makaranta tare da 'ya'yan shi. "_

      _"Haifaffiyar Jahar Kebbi kuma 'yar asalin garin Fulani, waton ƙauyen Ɗakin Gari. Na taso a garin Kebbi tare da mahaifina kafin Allah ya yi masa rasuwa. Na ci gaba da zama a garin Kebbi hannun Baba Ali cikin unguwar Aleru Quarters har na kammala karatuna a matakin digiri. Inda na yi Federal staff school nursery, primary and secondary. Sannan na ci gaba da karatun jami'a a Federal University Birnin Kebbi "_

           _"Mahaifiyata 'yar asalin jahar Sokoto ce. A ƙaramar hukumar wamakko lokal government. Jefi-jefi ina kai mata ziyara a duk lokacin da na samu sarari, sai dai ba na daɗewa idan ba babban hutu aka samu a makaranta ba."_

        _"A irin wannan ziyarar da nake kai wa Ummata a garin Sokoto na haɗu da Mukhtar har Allah ya ƙaddara aure tsakanina da shi. Sai dai kafin auren ya tabbata sai da aka yi ɗan ƙaramin gumurzu."_




Ni ma dai a matse nake da na ji tarihin aurenki da Mukhtar da wannan gumurzun😅


No comments

Powered by Blogger.